Quantcast
Channel: MUJALLARMU
Viewing all 3050 articles
Browse latest View live

KARANTA KAJI: KASAR SAUDIYYA TA HARAMTAWA ‘YAN KASAR QATAR SAMA MUTUM 700 AIKIN HAJJI DA UMRAH

$
0
0

Kasar Saudiyya Ta Haramtawa Wasu ‘Yan Kasar Qatar Aikin Hajji Da Umrah.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

A dalilin yanki hulda tsakanin kasar saudiyya da kasar Qatar ya jefa wasu ‘yan kasar dake zaune a kasar ta saudiyya da masu aikin hajji tsaka mai wuya.

A wani Rahoho da jaridar kasar Qatar ta fitar wani shugaban kwamitin kare hakkin dan adam  Ali Ibn Sumaikh ya bayyana rashin jindadin sa game da yadda yan kasar ke fuskantar barazanar hana su aikin hajji da umrah.

Kwamitin yace a Rahoto da suka samu daga kasar Saudiya alamu na nuna cewa akallah sama da mutane 700 ne aka hana gudanar da aikin hajji da umrah acikin kwanaki 5.

Abaya dai munji cewa kasar ta Saudiyya ta haramta sa rigar kungiyar kwallon kafa ta Barcelona a kasar ta Saudiya mai dauki da sunan Kasar Qatar,wanda hakan yasu janyo kuce kuce a tsakanin kasashen biyu.

 

The post KARANTA KAJI: KASAR SAUDIYYA TA HARAMTAWA ‘YAN KASAR QATAR SAMA MUTUM 700 AIKIN HAJJI DA UMRAH appeared first on MUJALLARMU.


SANATA DINO MELAYE YAYI SANADIYYAR MUTUWAR MUTANE 5 HAR LAHIRA

$
0
0

Rikicin Dino Melaye Da Matasan Jihar Kogi Yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 5.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Jiya mukaji cewa matasan jihar Kogi sunyi wata kazamar zanga zanga,wanda adalin haka yasa mutane 5 rasa rayukan su.

A Rahotanni da muka samu sun nuna muna cewa Sanata Dino Melaye yayi sanadin mutuwar wasu matasa 5 a zanga zangar.

Rigimar ta biyo baya ne bayan Dino Melaye yaje wata kwaleji dalibai dake jihar domin ganawa da wasu daga cikin magoya bayan sa,tsayawar sa keda sai wasu ‘yan bindaga suka kawo masa farmaki da shirin halaka sa.

Sanata Dino Melaye dai ya tsallake rijiya da baya,amma anyi nasarar kashe matasa 5 a rikicin tare da kona motoci biyu daga cikin motocin Sanata.

A Cewar Sanata yace yana zargin Gwamnan Jihar Kogi da shirya masa wata kullalliya domin ganin bayan sa.

The post SANATA DINO MELAYE YAYI SANADIYYAR MUTUWAR MUTANE 5 HAR LAHIRA appeared first on MUJALLARMU.

GWAMNA AYO FAYOSE YA BUKACI GWAMNATIN TARAYYA TASA BAKI WAJEN SULHU TSAKANIN KABILAR IGBO DA ‘YAN AREWA

$
0
0

Gwamna Ayo Fayose Ya Bukaci Gwamnati Ta Sasanta Rikicin ‘Yan Kabilar Igbo Da Arewa.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Kamar yadda muka sani cewa gwamna Ayo Fayose na Jihar Ekiti Gwamna daya saba fadin ra’ayinsa a kafafen yada labarai akan siyasar kasar nan musamman kan shugaba Buhari.

A yau dai Dandalin Mujallarmu.Com ta samu labarin cewa Ayo Fayose ya kuka abisa ganin yadda abubuwa keta faruwa tsakanin ‘yan kabilar Igbo da ‘yan Arewa,inda sanadiyyar haka yasa Ayo Fayose yake mai shawartar gwamnatin tarayya data bakinta wajen ganin an shawo kan matsalar dake faruwa a yankuna biyu domin a samu sulhu tsakani.

Ayo Fayose ya kara da cewa wannan abin kunya ne ace ‘yan kasa na irin wannan duk da cewa hakan na faruwa a wasu kasashe daban,a cewar sa yana mai jan hankalin matasan biafra da su gane cewa yau shekaru hamsin 50 kenan da kafuwar biafra saboda haka wancan qarni ya riga daya wuce.

The post GWAMNA AYO FAYOSE YA BUKACI GWAMNATIN TARAYYA TASA BAKI WAJEN SULHU TSAKANIN KABILAR IGBO DA ‘YAN AREWA appeared first on MUJALLARMU.

BA DAI DAI BANE ACE SHUGABAN KASA YA NADA SHUGABAN HUKUMAR ZABE-Inji Farfesa Jega

$
0
0

Bai kamata shugaban kasa ya nada shugaban hukumar zabe ba – Jega.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

A duk lokacin zabe, ana samun kiki-kaka kan ‘yancin hukumar zabe Najeriya Shugaban kasa ya ki yarda da hanin cewa fada ta nada shugaban zabe.

Kudin INEC a CBN ake ajiye shi A laccar da Farfesa Attahiru Jega ya bayar a Kano, a Mambayya majalisa, mai taken ‘Zabe da Adalci’, ya yi kira da a aiwaar da duk kudure-kudure da kwamitin Justice Uwais ya gabatar wa fadar shugaban kasa, kan batun damar nada shugaban hukumar zabe.
A kudurin dai, kamata yayi hukumar zabe ta zama mai cin gashin kanta ta ko wanne fanni, don tabbatar da adalci, da ingattacen kuma karbabben zabe.
A yanzu dai ana nadin shugaban hukumar ne daga fadar shugaban kasa, wanda hakan ke sa ana iya ganin kamar wasu zasu iya amfani da damar domin dora wanda zai yi musu aiki.
Jega Farfesan ya buga misali da kasar Ghana, inda ya ce: “ko a can ma, duk da zabe na kyau, shugaban kasa ne ke nadin, sai dai idan aka nada baya sauka sai ya kai sahekarun ritaya ta ma’aikaci.
“Amma an sami ci gaba, inda a yanzu haka, kudaden hukumar suna zaune ne a babban bankin Najeriya na CBN, kuma muddin shugaban kasa ya rattaba hannu ya saki kudin, to hukumar ce kadai mai yadda zata yi da kudin ta, ba tare da tsangwama ba.
” Ana dai shirin fuskantar zabe a cikin shekara mai zuwa, bayan da aka sami rabin wa’adin shekarun gwamnati mai ci a yanzu.

The post BA DAI DAI BANE ACE SHUGABAN KASA YA NADA SHUGABAN HUKUMAR ZABE-Inji Farfesa Jega appeared first on MUJALLARMU.

SHUGABANNIN TSARO NA GANAWAR SIRRI DA ‘YAN MAJALISU

$
0
0

Shugabannin hukumomin tsaro na ganawar sirri a majalisar dokoki.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Shugabannin hukomomin tsaron tarayya da ministocin tsaro da harkokin cikin gida na ganawa da majalisan wakilan tarayya , jaridar Channels na bada rahoto.
            
Rahoton na cewa babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin majalisan wakilan na cikin ganawa da yan majalisu,Dandalin Mujallarmu.com ta bada rahoton cewa ministocin da shugabannin jami’an tsaron zasuyi bayani gayan majalisa akan matakan da suke dauka wajen dakile rashin tsaron da yayi katutu a kasa.
Yan majalisan sunyi sun jawo hankali akan yawaitan rashin tsaro wanda ya kunshi garkuwa da mutane da kuma fashi da makami.
A wata jawabi da Hon Babatunde kolawole ya gabatar inda abokan aikinsa irinsu Ado Dogowa, Emmanuel Orker-Jev da Adam Jagaba suka marawa bayam yan majalisan sunyi kira ga gwamnatin tarayya tayi fito na fito da garkuwa da mutane a fadin tarayya.

The post SHUGABANNIN TSARO NA GANAWAR SIRRI DA ‘YAN MAJALISU appeared first on MUJALLARMU.

HUKUMAR EFCC NA CIGABA DA BINCIKEN MAJALISAR WAKILAI GAME DA ALMUNDAHA A KASAFIN KUDIN 2016

$
0
0

EFCC ta shiga bincike akan badakalar kasafin kudin 2016, ta gayyaci Jibrin.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

 Hukumar yaki da rashawa ga bukaci dakataccen sanata Jibrin Adulmumin ya bayyana gabanta domin kara mata haske akan badakalar kasafin kudin 2016 da yace anyi almundahana.
    
Gayyatar tazo ne bayan wani nazari da hukumar na kokarin ta gano wata almundahana da akace mata an tamka a kasafin kudin.
Hukumar ta EFCC tA aikawa da dakataccen sanatan da wasika dake dauke da kwanan wata 9 ga watan yuni,yanzu haka dai hukumar yaki da rashawa ta shiga fara binciken da aka sanar da ita game majalisar ta wakilai tayi a kasafin kudin 2016.
Hukumar ta bukaci cewa lallae ya zama wajibi ta gayyaci Jibrin ofishin ta dake wuse 2 lamba 5 abuja a yau talata domin amsa wasu tambayoyi, a misalin karfe goma na safiyar yau
A Wata hira da Jibrin yayi da manema labarai yace yayi farincikin wannan gayyata da hukumar EFCC ta aiko masa,domin tazo masa adai dai sannan kuma yana fatar al’umma idan sunji korafen da yake dashi akan yan majalisar toh sai su dauki matakin daya kamata.
A wata takarda da ya fitar ga manema labarai, Abdulmuminu Jibrin ya ce ya ji dadin wannan gayyata, saboda ta zo ne a dai dai lokacin da mutane da dama suka hakura da fatan cewa za a dauki mataki akan korafe korafen.
A karshe Jibrin yace yana mai yabawa irin tsantsar aikin da Ibrahim magu keyi abisa gaskiya da amanah.

The post HUKUMAR EFCC NA CIGABA DA BINCIKEN MAJALISAR WAKILAI GAME DA ALMUNDAHA A KASAFIN KUDIN 2016 appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: MANYAN FINA FINAN HAUSA GUDA 7 DA ZASU FITO A RANAR SALLAH

$
0
0

Fina-Finan Kannywood Guda 7 Da Zasu Fito Da Karamar Sallah.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

  

Manya manyan furodusosin masana’antar shirya fina finai ta Kannywood sun shirya fito da wasu daga cikin fina finan da aka dade ana tsumayi a lokacin shagulgulan sallah karama.

Rahama Sadau za ta fitar da fim din ta mai suna Rariya wanda Yasin Auwal ya bada umarni a ranar 26 ga watan nan.

Fim din Ali Nuhu Mansoor shi ma ana tsammanin zai fito a daidai lokacin da ake bukukuwan Sallar.

haka zalika na Abubakar Mai Shadda Kanwar Duba rudu, wanda Ali Nuhu da Rahama Sadau suka fito a matsayin ya da kanwa.

Sai kuma fin din Zaharaddeen Sani Abu Hassan wanda ya bada labarin tabargazar da wata kungiyar ta’addanci ta yi a gari kafin a karshe sojoji su murkushe ta.

Sauran da ake tsammani za su fito a lokacin sun hada da BintotoSultana da Munaqisa

An dai dakatar da fitowar fina finan saboda zagayowar watan Ramadan.

Wannan shi ne karon farko a masana’antar da za a haska manyan fina finai irin wadannan a lokaci daya a sinima.

The post KARANTA KAJI: MANYAN FINA FINAN HAUSA GUDA 7 DA ZASU FITO A RANAR SALLAH appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: AMFANIN SHAN RUWA 6 A JIKIN DAN ADAM

$
0
0

Lafiya uwar jiki : Amfanin yawan shan ruwa 6 ga jikin dan Adam.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Jaridar NAIJ.com ta tattaro muku muhimman amfanonin ruwa 6 ga ruhin dan Adam a koda yaushe. Masu magana sukace ruwa baka da makiyi,Shi ruwa wani sinadari ne da Allah mai jinkai ya baiwa bayinsa cikin sauki kuma a yawaice.

Amma da yawanmu bamu san dimbin amfaninshi ba face gusar da kishi da kuma ayyukan yau da kullum.

Ga amfanin ruwa ga jikinmu:
1. Rage kiba Shi ruwa bai da mai, bai da siga, kana kuma bai da sinadarin kalori, saboda haka shan shi koda yaushe yakan taimaka wajen rage kibar jiki.
2. Lafiyar zuciya Game masu ilimin lafiyar zuciya, ruwan kan rage iwuwan samun ciwon zuciya da 41 cikin 100
3. Karfin jiki Ruwa kan taimaka wajen karfin jiki saboda rashin shan sa kan kashe jikin mutum, ya maishe shi a gajiye. Lafiya
4. Warkar da ciwon kai Hasali abinda ke kawo ciwon kai shine rashin shan isasshen ruwa
5. Kyawun fatar jiki Ruwa kan sa fatar jikin mutum ta dinga kyau tana kyalli a koda yaushe
6. Cutan daji Ruwan kan rage yiwuwan kamuwa da cutan dajin mafitsara da kasha 50 ciki 100

The post KARANTA KAJI: AMFANIN SHAN RUWA 6 A JIKIN DAN ADAM appeared first on MUJALLARMU.


KARANTA KAJI: ANA SHIRIN SOKE AMFANI DA NIKABI GA MATA A WATA KASA

$
0
0

         Ana shirin haramta amfani da Nikabi a wata kasa.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Ana yunkurin haramta Hijabi a Kasar Norway masu amfani da nikabi za su fuskanci barazana haramcin dai zai shafi kaf daliban makaranta Kasar Norwegia za ta hana Daliban makaranta sa nikabi.
     
A jiya Gwamnatin kasar ta fara shirin kawo wannan doka Nikabin na hana dalibai daukar karatu Inji Ministan ilmi Ana shirin haramta amfani da Nikabi a wata kasa Za a hana sa Nikabi a Kasar Norway.
Gwamnatin Kasar Norway na shirin haramta amfani da nikabi a Makarantun firamare da sakandare da ma na gaba da su,Gwamnatin na kukan cewa irin wannan sutura na hana dalibai fahimtar karatu da kyau.
Nikabi na hana Dalibai daukar karatu Inji Gwamnati Ministan Ilmi na kasar Torbjorn Roe Roe Isaksen ya bayyana wannan a jiya Litinin. Ana dai shirin kafa dokar da za ta haramta amfani da nikabin da ke rufe fuska nan da zuwa shekara mai zuwa wanda wannan dai na iya kawo rikici da Musulman kasar.
A bara ne Jaridar Daily Mail ta rahoto cewa ana yunkurin hana amfani da dogon Hijabi da ake kira burqah a Kasar Jamus.
Shugaban Kasar Jamus, Angela Merkel tace bai dace ace ana amfani da burqah a Kasar ba damin Kasar Kirista ce.

The post KARANTA KAJI: ANA SHIRIN SOKE AMFANI DA NIKABI GA MATA A WATA KASA appeared first on MUJALLARMU.

KOTUN KASAR TUNISIA TA DAURE WANI MATASHI SABODA YA BUSA SIGARI A WATAN RAMADANA

$
0
0

     An ɗaure shi saboda ya busa sigari a watan Ramadana.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Alkali ya yanke ma matashi hukuncin zaman gidan kaso saboda sha sigari  Matashin ya busa sigari ne a gaban kotu a kasar Tunisia Wata kotun kasar Tunisia ta aika da wani matashi gidan kasa sakamakon kama shi da tayi da laifin shan sigari a bainar jama’a a yayin gabatar da Azumin watan Ramadana.
     
 Jaridar Punch ne ta dauko rahoton inda tace an kama mutumin ne yana shan sigari a wajen Kotu, inda nan da nan aka sanar da Yansanda suka yi awon gaba da shi, kuma ba tare da bata lokaci ba suka mika shi gaba alkali.
Sai dai kotu ta baiwa mutumin daman daukaka kara a kwanaki 10. Ko a ranar 1 ga watan Yuni sai da aka daure mutane hudu zuwa zaman watan guda a gidan yari sakamakon cin abinci a bainar jama’a, kamar yadda majiyar Dandalin Mujallarmu.com ta ruwaito An ɗaure shi saboda ya busa sigari a watan Ramadana Wannan hukuncin kotu ya biyo bayan wani gangamin zanga zanga da wasu mutanen kasar suka gudanar a ranar Lahadi 11 ga watan Yuni domin neman a basu daman su ci abinci a bainar jama’a a watan Ramadana.

The post KOTUN KASAR TUNISIA TA DAURE WANI MATASHI SABODA YA BUSA SIGARI A WATAN RAMADANA appeared first on MUJALLARMU.

SAI MUN KONE DUKIYOYIN MU KAFIN MUBAR AREWA-INJI KABILAR IBO

$
0
0

Korar kabilar Ibo: ‘Sai mun kone duk dukiyarmu zamu bar arewa’.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

An shawarci kabilar Ibo da su kwashe arzikinsu in har ta tabbata korar su za ayi – An basu shawara su kone abun da ba zai dauku ba An ji tsit, batun kame samarin arewa da suka yi wa kabilu barazana Cif Nathaniel Amaechi, shugaban kabilar Ibo mazauna jihar Ekiti, ya yi tir da kiraye-kiraye da ake wa juna tsakanin kabilun kasar nan, inda yace wannan wani abun kunya ne, musamman ganin ba’a kama kowa ba a lamarin.
          
 Cif Amaechin, yana magana ne kan batun wai wa’adin korar kabilar Ibo daga arewa, inda yace yayi mamaki manyan arewa da manyan kasarnan basu furta komai kan batun ba, ba kuma su nuna ko-in-kula ba.
Yace mutane irin su shugaba Obasanjo, IBB da ma gwamnatin tarayya basu ce uffan ba ko tir da batun, wannan abin takaici ne, a cewarsa.
Ya kuma yi kira ga kabilar Ibo da su yi zamansu a inda duk suke ba tare da tsangwama ba, ya kuma ce lallai a zauna lafiya, amma idan aka ce wa’adin da gaske ne, to “kabilar Ibo su sayar da duk dukiyoyinsu, su kuma kone sauran da baza su iya diba ba, su mayar da arewar hamada, kamar yadda suka same ta.”
A cewarsa, muddin hakan ya auku, kabilar Ibo ita ce zasu yi nasara, inda yace arewar ce zata yi asara mai yawa, saboda dumbin dukiya da kadarori na tiriliyoyin nairori da suka zuba jari a arewar.

The post SAI MUN KONE DUKIYOYIN MU KAFIN MUBAR AREWA-INJI KABILAR IBO appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: ASHE ZUWAN AISHA BUHARI LANDAN BA’A BARI TA GANA DA SHUGABA BUHARI BA

$
0
0

Labari da dumu dumi: Ashe ba’a bari Aisha Buhari ta gana da maigidanta ba a Landan – Sahara Reporters.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Rahoto ya nuna cewa shugaba Buhari bai samu daman ganin uwargidansa ba a ziyarar da ta kai masa Landan Rahoton tace rashin lafiyan shugaban kasan tayi tsananin Jaridar Sahara Reporters ta bada rahoton cewa ba’a bari shugaba Buhari ya gana da uwargidansa, Aisha Buhari ba yayinda ta kai masa ziyara Landan.
         
Game da cewar Sahara Reporters, majiya ta bayyana cewa da yawa daga cikin ma’aikatan Buhari basu san inda yake har da masu gadinsa.
Sahara Reporters Kamfanin jaridan ta kara da cewa shugaban kasa Buhari har ila yau bai yi magana da Farfesa Yemi Osinbajo a wayan tarho ba tun lokacin ya fita Najeriya jinya.
Wata rahoton tace miyagu sun hana mutane kusanta Buhari saboda dakile fitar wasu maganganu saboda ana zargin cewa shugaban kasa na fama da ciwon daji.

The post KARANTA KAJI: ASHE ZUWAN AISHA BUHARI LANDAN BA’A BARI TA GANA DA SHUGABA BUHARI BA appeared first on MUJALLARMU.

ANYI ZAMAN SULHU TSAKANIN DATTAWAN AREWA DA OSINBAJO-(Hotuna)

$
0
0

Zaman tattaunawa tsakanin shugabannin Arewa da Osinbajo (HOTUNA).

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Anyi gemu da gemu tsakanin Osinbajo da shuwagabannin Arewa a fadar shugaban ƙasa Osinbajo yace zasu yi maganin duk wani da aka kama yana yin kalaman batanci Mukaddashin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo yace gwamnatin Najeriya ba za tayi kasa a gwiwa ba wajen yin maganin duk wani da aka kama yana yin kalaman batanci da ka iya haifar da tarzoma.
          
Osinbajo ya bayyana haka ne yayin ganawa da shuwagabannin yankin Arewacin kasar nan a fadar shugaban kasa, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.
Wannan gargadi baya rasa nasaba da wa’adin tattara kayanku da wasu matasan yankin Arewa suka baiwa yan kabilar Igbo.
                                 
“Gwamnati ba zata yi sakwa sakwa ba da duk wani yunkurin tayar da tarzoma a kasar nan domin ba’a san karshen rikici ba.” Inji shi.

The post ANYI ZAMAN SULHU TSAKANIN DATTAWAN AREWA DA OSINBAJO-(Hotuna) appeared first on MUJALLARMU.

WATA YARINYA ‘YAR SHEKARA 17 TA KASHE MUTUMIN DA YAYI KOKARIN YI MATA FYADE

$
0
0

Wata ‘Yar Shekaru 17 Ta Kashe Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Yi Mata Fyade

Wata ‘Yar Shekaru 17 Ta Kashe Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Yi Mata Fyade

An gurfanar da wata matashiya mai shekaru 17 a gaban kuliya a sakamakon kashe wani saurayi da ya yi yunkurin yi mata fyade a kasar Afrika ta Kudu.

Rahotanni sun bayyana cewa saurayin mai shekaru 21 ya farwa matashiyar ne yayin da take kan hanyar ta na zuwa wani guri da ba a bayyana ba, inda suka fara kokawa har ta ci karfinsa, ta daba masa wuka.

Bayan da aikata abun ne ta mika kanta ga ‘yan sanda.

‘Yan sanda sun bayyana cewa lokacin da ta mika kan na ta, tana cikin rudani. A don haka ana bata duk wata kulawa da ya kamata.

Haka kuma sun ce ba za su bayyana sunan ta ba saboda a karkashin dokokin kasar, har yanzu yarinya ce karama.

Kotun za ta kara sauraran karar a yau, 14 ga watan Yuni, inda matashiyar za ta fada wa kotun cewa, abun da ta aikata ta yi ne domin ta kare kanta.

Ita kuwa kotun za ta dora maganar ta ta akan mizanin shari’a ta yanke hukunci.

Fyade dai ya na daya daga cikin abubuwan da ke ciwa mutanen Afrika ta Kudu tuwa a kwarya, inda ake samun fiye da 60,000 a kowacce shekara.

Da yawa a cikin matan na rasa rayukan su a sakamakon haka.

The post WATA YARINYA ‘YAR SHEKARA 17 TA KASHE MUTUMIN DA YAYI KOKARIN YI MATA FYADE appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: GWAMNATIN JIHAR SOKOTO TA AIKI DA MALAMAN ADDINI 90 KASA MAI TSARKI DON YI WA SHUGABA BUHARI ADDU’A

$
0
0

Tambuwal ya aika Shehunnan Malamai 90 Makkah don yi ma Najeriya addu’a.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Jihar Sakkwato ta kammala shirin aikawa da wasu Maluma kasar Saudiya Za’a aika da malaman ne domin gudanar da aikin Umarah saboda wasu dalilai Ma’aikatar kula da addini na jihar Sakkwato ta kammala shirin aikawa da wasu manya manyan  Maluma kasar Saudiya domin gudanar da aikin Umarah saboda wasu dalilai.
       
 kamar yadda Rariya ta ruwaito. Majiyar Dandalin Mujallarmu.com ta bayyana cewar gwamnatin jihar ta bayyana dalilin tura malaman aikin Umarah shine domin suyi ma shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’ar samun lafiya.
Bugu da kari ana sa ran malaman zasu yi ma jihar Sakkawato addu’an samun cigaba mai daurewa da zaman lafiya, har ma su yi ma kasa gaba daya addu’a.
Tambuwal A ranar Laraba 14 ga watan Yuni ne ake sa ran Malaman zasu tashi zuwa kasa mai tsarki don gabatar da ibada da addu’o’in.
Gwamnatin jihar Sakkwato karkashin jagorancin Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ta dauke ma malaman dawainiyar gidajensu, inda aka baiwa kowanne malami N50,000 domin lamurran gidansa a yayin dayake Saudiya.

The post KARANTA KAJI: GWAMNATIN JIHAR SOKOTO TA AIKI DA MALAMAN ADDINI 90 KASA MAI TSARKI DON YI WA SHUGABA BUHARI ADDU’A appeared first on MUJALLARMU.


IDAN SHUGABA BUHARI BAZAI YI TAKARA BA A ZABEN 2019, WA ZAKA ZABA DAGA AREWA?

WASU DALIBAI SUN BAIWA GWAMNA EL’RUFAI WA’ADIN SATI UKU A KADUNA

$
0
0

        An baiwa El-Rufai wa’adin sati uku shima a Kaduna.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

A Kaduna, an rufe makarantun kudancin Kaduna tsawon watanni – Wasu dalibai sun baiwa gwamnati sati uku ta bude makarantun ko taga abun da suke niyyar yi  a Kaduna dai ana samun sabani tsakanin kabilu da addinai a lokuta da dama.
A taro da manema labarai da suka yi, kungiyar samarin kudancin kaduna ta Southern Kaduna Youth Forum, ta fitar da sanarwar baiwa gwamna wa’adin sati uku ko ya fitar musu da jaddawalin sake komawa makaranta ko kuma ya fuskanci hushinsu.
A cewar wata Sanarwar ta bakin Ezekiel David, sakataren kungiyar ya bayyana cewa: “Albarkacin watan Ramadana, mun dauki aniyar kwato wa mutanen yankin mu darajar su don haka mun yanke wa gwamna El-Rufai sati uku ko ya bude mana makaranta mu dena zaman banza, ko ya fuskanci fushin mu.
“Abin mamaki sai ace wadanda suke cewa su ne masu kishin ilmi a kasa amma sun ware wani bangare na al’ummarsu, sun hana su ilmin. Banda Malam Nasir El-Rufai, babu wanda ya san wannan dalili.”
Kwamared Galadima Jesse, Shugaban kungiyar ya bayyana cewa an rufe makarantun Noma na jami’ar Kasu da ke yankin, an kuma rufe kwalejin koyan ilimin jinya da kwalejin ilimi a kafanchan, tun lokacin rikicin kabilanci a bara. Kuma babu ranar budewa.
A cewar gwamnati dai, rikicin kabilanci ne ya jawo aka rufe wasu makarantun. An bude wasu makarantun, wasu kuwa har yanzu a rufe suke. Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

The post WASU DALIBAI SUN BAIWA GWAMNA EL’RUFAI WA’ADIN SATI UKU A KADUNA appeared first on MUJALLARMU.

SHIRU KAKE JI: HAR YANZU SHUGABA BUHARI BAI YI MAGANA DA OSINBAJO BA TUN KOMAWAR SA KASAR LANDAN

$
0
0

Tun lokacin da Buhari ya tafi Landan, Farfesa Osinbajo bai yi magana da shi ba – Rahoton Sahara Reporters.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Shugaba Muhammadu Buhari ya koma kasar Landa jinyan bayan dawowansa a wata Mayu. amma wasu maganganu na bayyana game da lafiyar jikinsa. Majiya ta bayyanawa sahara Reporters cewa daya daga cikin makusantan Buhari ya kira mukaddshin shugaban kasa cewa ya saurari kira daga Buhari amma har yau bai samu kiran ba.
                               
Dandalin Mujallarmu.com ta tuna cewa wani jigon jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Orji Uzor Kalu, yace Buhari ya samu lafiya kuma zai dawo Najeriya ranan 11 ga watan Yuni.
Amma ya bayyana cewa Kalu karya kawai yakeyi sabod babu lokacin da shugaba Buhari ya kirashi.
Sahara Reporters ta karashe da cewa shugaba Buhari bai iya sadarwa da mutane kuma ma’aikatansa biyu kadai ke tare da shi ;Tunde Saburi da Sarki Abba.

The post SHIRU KAKE JI: HAR YANZU SHUGABA BUHARI BAI YI MAGANA DA OSINBAJO BA TUN KOMAWAR SA KASAR LANDAN appeared first on MUJALLARMU.

GARABASA: YADDA ZAKA SAYI 1GB DATA AKAN N200 A LAYIN KA NA ETISALAT

$
0
0

GARABASA: YADDA ZAKA SAYI 1GB DATA AKAN N200 A LAYIN KA NA ETISALAT

Kamfanin sadarwa na Etisalat ya fitar da wata garabasa a cikin wannan watan na ramadan wanda mutun zai mallaki data kimanin 1gb akan N200.

Wannan wata garabasa ce da kamfanin ya fito da ita wacce zaka iya komai da ita.

Domin samun wannan garabasa

Ka tabbatar kana da katin N200  a layin ka na Etisalat Sai Ka Danna *929*10#

Amma fa wannan garabasa ba ta kowa da kowa bane sai mai rabo.

 

Allah sa a dace.

The post GARABASA: YADDA ZAKA SAYI 1GB DATA AKAN N200 A LAYIN KA NA ETISALAT appeared first on MUJALLARMU.

SAKAMAKON CIN GURBATACCEN ABINCI YA KWANTAR DA ‘YAN GUDUN HIJIRA DA DAMA

$
0
0

Gurbataccen abinci ya kwantarda daruruwan ‘yan gudun hijira.

Marubuci:Haruna Sp 

Kungiyar kula da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa ta bada rahoton cewar kimanin muatne 752 suka kamu da rashin lafiya. – Kungiyar kula da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa ta bada rahoton cewar kimanin muatne 752 suka kamu da rashin lafiya.
        
Daga cikin wannan adadi mutum 312 aka kwantar a asibitotci, kana akalla wasu mutane biyu suka mutu da suka hada da wani yaro da wata mace sakamakon cin abincin daya lalace a wani sansanin da aka ajiye wadanda suka rasa gidajensu a wajen birnin Mosul na kasar Iraq.
Dandalin Mujallarmu.com ta samu labarin cewa kakakin kungiyar ta kula da bakin hauren Joel Millman ya fada a shekaranijya Litinin cewar wani dan kwangila ne ya kawo abinci da misalign karfe hudu na rana don buden baki na watan Ramadana da suka saba yi da za a raba abincin a daidai karfe 7:30 na yamma.
Kakakin yace hukumomi na binciken lamarin don gano inda gurabataccen abinci ya fito ko kuma abinci ya gurbace ne tsakanin lokacin da aka kawo da lokacin da aka fara raba shi. Bayan an basu abincin, mazauna sansanin sun ce mutane da dama sun kamu da ciwo kana kuma hukumomi basu da isasshen motocin kwasan marasa lafiya inda suka cika motocin bus suka makil da mutane.

The post SAKAMAKON CIN GURBATACCEN ABINCI YA KWANTAR DA ‘YAN GUDUN HIJIRA DA DAMA appeared first on MUJALLARMU.

Viewing all 3050 articles
Browse latest View live


<script src="https://jsc.adskeeper.com/r/s/rssing.com.1596347.js" async> </script>