Quantcast
Channel: MUJALLARMU
Viewing all 3050 articles
Browse latest View live

DANDALIN KANNYWOOD: JARUMI SULEIMAN BOSHO ZAI FUSKANCI MUMMUNAN HUKUNCI KAN OVER ROLE DAYA KE YI-Inji Moppan

$
0
0

Dandalin Kannywood: Fitaccen jarumi Suleiman Bosho zai fuskanci mummunan hukunci.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Kungiyar ladabtar da jarumai maza da mata Moppan ta fitar da wata sanarwa a safiyar yau talata cewa: zata hukunta jarumin barkwanci Sulaiman Bosho bisa laifin dori akan abinda darakta ya umarce shi wato over role kenan.
Acewar Moppan: “Mun jima muna ganin kura kuran da Bosho Yake Yi acikin fim, mun kira shi dan ya gyara amma ya kasa gyarawa.” “Mun tuhumi daraktocin da suke da suke sa shi acikin fim amma sunce, su basu ga laifi ko munin kalamansa ba.
Dan hakane muka yanke hukuncin hukunta daraktocin da kuma shi jarumi Bosho”. Inji Moppan. Dandalin Mujallarmu.com ta samu labarin cewa hukuncin da za’ayi jarumi Bosho akwai tara wanda aka ci Bosho dan wannan ya zama izna agare shi dama daraktocin da suke bashi umarnin furta kalaman da basu dace ba.
Da muka tambayi Bosho akan da wacce fuska ya kalli wannan hukunci? Sai ya amsa da cewa: “Wannan hukunci son ransu suka aikata, domin mutane sune ya kamata su gane laifin da muka aikata basu ba, domin mutane sune masu kallon mu, sune alkalai ba Moppan ba.”

The post DANDALIN KANNYWOOD: JARUMI SULEIMAN BOSHO ZAI FUSKANCI MUMMUNAN HUKUNCI KAN OVER ROLE DAYA KE YI-Inji Moppan appeared first on MUJALLARMU.


SAKE SABON AURE YASA NA SAMU NATSUWA YANZU-Inji Ahmad Musa

$
0
0

Na Samu Nutsuwa Yanzu, Inji Ahmed Musa Game Da Sabon Auren Shi

Na Samu Nutsuwa Yanzu, Inji Ahmed Musa Game Da Sabon Auren Shi

Dan wasan gaba na kungiyar Super Eagles da Leicester City, Ahmad Musa ya yi tsokaci akan sabon auren da ya yi a kwanakin baya.

A wata hira da ya yi da jaridar Complete Sport, Ahmad ya bayyana cewa yanzu ya na cikin farin ciki kuma ya samu nutsuwa a wajen buga wasannin sa.

A cewar shi “Aure ba sabon abu bane a gurina, kuma na yi imanin na yi abunda ya kamata ne a lokacin da ya kamata. Abunda ya wuce ya wuce”

A watan da ya gabata ne dai Ahmad Musa ya auri amaryar shi Juliet Edeh bayan ya saki matar shi ta shekaru hudu kuma uwar ‘yayan shi biyu mai suna Jamila.

Rahotanni sun bayyana cewa zaman Ahmad da Jamila ya ki dadi ne a sakamakon kin yarda da ta yi ya auro Juliet.

 

Ahmad dai bai tabuka abun kirki ba a zangon wasanni na daya na Fremiyar kasar Ingila, inda ya ci kwallaye hudu kacal a wasanni 32.

The post SAKE SABON AURE YASA NA SAMU NATSUWA YANZU-Inji Ahmad Musa appeared first on MUJALLARMU.

KALLI YADDA SHUGABA BUHARI YA KARRAMA WANI INYAMURI GURGU DAN BAUTAR KASA-(Hotuna)

$
0
0

Yadda Buhari ya karrama wani Inyamuri gurgu dan bautan ƙasa.

Marubuc:Haruna Sp Dansadau

Shugaba Buhari ya karrama wani gurgu dan bautan kasa – Wannan karramawa ta wakana ne a shekarar 1984 A zamanin mulkinsa na Soji, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama wani gurgu dan bautan kasa, Chukwuemeka Oliwe sakamakon wani hazaka da ya nuna.
               
 Jaridar Abiyamo ta ruwaito, shugaba Buhari ya karrama wannan gurgu ne a shekarar 1984, inda ya lashe lambar yabo da kyautar da shugaban kasa ke baiwa duk wani dan bautan kasa da yafi nuna kwazo a yayin da gudanar da hidimar kasa.
 Wannan bikin karrama yan bautar yi ma kasa hidima na wannan shekara ya gudana ne a dakin taro na kasa dake Legas.
Dandalin Mujallarmu.com ta ruwaito a wasu lokutan akan karrama yan bautan kasa ne da suka fi amfani ga jama’a da suka yi ma hidiman, ta hanyar gina hanya, samar da ruwan sha, asibiti da sauransu.
Anan ma wani hoton Buhari ne tare da yan hidimar kasa a garin Daura bayan ya lashe zaben shugabancin kasar nan a shekarar 2015.
Yadda Buhari ya karrama wani Inyamuri gurgu dan bautan ƙasa Buhari da yan hidimar ƙasa.

The post KALLI YADDA SHUGABA BUHARI YA KARRAMA WANI INYAMURI GURGU DAN BAUTAR KASA-(Hotuna) appeared first on MUJALLARMU.

SO KARSEHN ZANCE: KARANTA KAJI YADDA WANI BATURE YA MUSULUNTA SABODA SOYAYYAR WATA MUSULMA

$
0
0

Bature Ya Musulunta Sanadiyyar Soyayya Karshe An Shafa Fatiha.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Michael mai shekara 29 dan asalin kasar Holland, ya hadu da Adin Lubi yar shekara 22 ne, yar kasar Indonesia.
                                 
Game da yandda suka hadu, Micheal yace ; “Nayi tunanin zai yi kyau inyi azumin Ramadana da Musulmai. Bayan bincikena a kafafen sada zumunta na yanar gizo, sai na samu Adin kuma na rubuta mata sako.
Abin mamaki, da wuri ta gayyaceni inzo in zauna tare da iyalinsu tsawon kwani 3 a Medan, Indonesia da azumi. Bature ya Musulunta sanadiyar soyayya da Musulma kuma a karshe an shafa Fatiha Bature ya Musulunta sanadiyar soyayya da Musulma kuma a karshe an shafa Fatiha “ Bari ma, sai da nayi makonni 3 a gida. Haka muka fara soyayya da ita.
                                
” “Yawancin masu karban bakoncina a Indonesia da Malaysia Musulmai ne. Basu ta bace mini in Musulunta ba, innama sun nuna min yadda suke rayuwarsu.”
“Dalilin da yasa na zabura kan neman ilimin addinin Musulunci kenan kuma na fara neman ilimi a Masallatan Kuala Lumpur da Jakarta.”
“Yayinda nike zuwa karatu, ban yi niyyan Musulunta ba. Kuma malamai ne sun san da hakan kuma basu damu ba.
Bayan makonnin neman ilimi, karatun AlKur’ani da kuma koyan Sallah, sai na fahimci cewa shiga addinin Musulunci ne yafi kyautata a rayuwa na.”

The post SO KARSEHN ZANCE: KARANTA KAJI YADDA WANI BATURE YA MUSULUNTA SABODA SOYAYYAR WATA MUSULMA appeared first on MUJALLARMU.

‘YAN AREWA ZASU SAKE ZABEN SHUGABA BUHARI KO AKAN KEKEN GURAGU YAKE YAWO-Inji Yakubu

$
0
0

‘Yan Arewa Za Su Sake Zaben Buhari Ko a Keken Guragu Ya Ke Yawo – Yakubu

‘Yan Arewa Za Su Sake Zaben Buhari Ko a Keken Guragu Ya Ke Yawo – Yakubu
 Daya daga cikin dattijan kungiyar Arewa Consultative Forum Mohammed, Alhaji Yakubu ya jaddada cewa ‘yan Arewa za su sake zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari a 2019 ko da ace a keken guragu yake yawo.

A wata hira da jaridar The Sun ta yi da shi, Yakubu ya ce ba zai shawarci Buhari ya sauka daga kan mulki ba.

Ya ce idan ba a manta ba, a lokacin da tsohon shugaban kasa Obasanjo ya cewa marigayi Umaru Musa ‘yar Adua ya sauka daga mulki saboda rashin lafiya, ya yi hira da jaridar, inda ya fadi iri wannan magana da yake yi a yanzu. Ya ce sai dai ba  samu sa’a ba ya rasu.

Ya kara da cewa bai kamata ace a kunyata Buhari daga ofishin sa ba ta hanyar matsa masa lamba sai ya sauka, A fadar shi “Hakan ba daidai ba ne, bai dace ba”

Ya ce muna da tsarin zabe, duk wanda bai son Buhari ya tsaya sai lokacin zabe tukunna ya nuna haka. “Amma matukar Buhari na da rai, bai kamata ya sauka daga mukamin sa ba” a fadar shi.

The post ‘YAN AREWA ZASU SAKE ZABEN SHUGABA BUHARI KO AKAN KEKEN GURAGU YAKE YAWO-Inji Yakubu appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: WANI DAGATACCEN SANATAN SHUGABA BUHARI YA FASA KWAI

$
0
0

Abun da dakataccen dan majalisa, Jibrin ya fada ma EFCC a lokacin tambayoyins.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Dan majalisa Abdulmumin Jibrin ya amsa gayyatar hukumar EFCC a ranar Talata – Ya amsa wasu tambayoyi da hukumar ta yi masa a kan wadanda ya zarga da zamba a kasafin kudi – Hukumar ta ce zata gayyaci wadanda aka zarga daya bayan daya.
            
A ranar Talata, hukumar yaki da cin hanci da rashawa wato EFCC ta yi ma tsohon dan majalisa Abdulmumin Jibrin, tambayoyi na kimanin sa’o’I biyar a babban ofishin ta dake Abuja. Jibrin ya isa harabar ofishin da misalin karfe 10 na safe, inda ya tsaka har karfe 3 na rana wanda daga bisani aka nemi ya tafi, jaridar Punch ta ruwaito.
An bukaci dan majalisan da yayi cikakken bayani tsarin kasafin kudi da kuma yadda wasu daga cikin abokan aikinsa suka sanya wasu ayyuka ta wasu kamfanoninsu. Abun da dakataccen dan majalisa, Jibrin ya fada ma EFCC a lokacin tambayoyinsa Abun da dakataccen dan majalisa, Jibrin ya fada ma EFCC a lokacin tambayoyinsa
“Jibrin ya zo a ranar Talata kamar yadda aka bukata. Ya kasance tare da mu daga karfe 10 na safe har 3 na rana. “Ya yi bayani a kan tsarin kasafin kudi da kuma yadda aka kara wasu alkalma a cikin kasafin kudin.
“Da dama daga cikin wadanda aka zarga suna da bayanai da dama da zasu yi. Zamu gayyaci wadanda aka zarga daban-daban,” cewar wani jami’I a hukumar EFCC.

The post KARANTA KAJI: WANI DAGATACCEN SANATAN SHUGABA BUHARI YA FASA KWAI appeared first on MUJALLARMU.

BATAN BASIRA YASA WASU JAMA’AR INDIA BAUTAR YARON DA AKA HAIFA DA BINDI-(Hotuna)

$
0
0

Jama’ar india na bautan wani yaro ‘mai bindi’ a kasar India (HOTUNA).

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

An haifi wani yaro a kasar India da bindi – Jama’a sun shiga harkar bautan wannan yaro Wani karamin yaro dan shekara takwas mai suna Dulha Singh da aka haifa da wani abu kamar bindi a bayansa ya samu mabiya masu bauta masa.
         
Bindin wannan yaron ya samu asali ne daga wani tarin gashi da ya fito ma yaron a bayansa, sa’annan iyayensa sun ce yanke wannan bindi ka iya zama mummunan laifi akan wanda zai iya zuwa da mummunan sakamako.
                              
A yanzu haka yan kauyen Amritsar, inda Dulha ke zaune da kawunsa suna tururuwa gidansa domin yi masa bauta, a yadda suke fada, sunce Dulha kwatankwancin ubangijin birai ne na addinin Hindu mai suna Hanuman.
Yaro ‘mai bindi’ Dayake yaro Dulha na sha’awar hawa bishiya da wasa a akai, yasa ya kara tabbatar ma yan kauyen cewa lallai shine ubangijin birai na addinin Hindu.
             
Wannan yasa yan kauyen suke ganinsa kamar wata rahama ne a garesu, shi yasa ma suke shafarsa domin samun tubarraki.
’ Wasu kuma bindin nasa suke tabawa domin samun babban tabarraki, da karama, innarsa tace “Jama’a da daman a zuwa ganinsa a kullum, sun yi amanna shine Hanuman Ji.”
Yaro ‘mai bindi’ tare da kawunsa da innarsa Sai dai Dandalin Mujallarmu.com ta ruwaito yaro Dulha baya jin komai a jikinsa, kuma baya damuwa da yadda jama’a ke son taba shi da taba bindin nasa, shi kam bai ma san dalilin da yasa jama’a ke son neman tubarraki a wajen sa ba.

The post BATAN BASIRA YASA WASU JAMA’AR INDIA BAUTAR YARON DA AKA HAIFA DA BINDI-(Hotuna) appeared first on MUJALLARMU.

KARANJI KAJI: DALILAN DA YASA KAMFANIN MTN DA AIRTEL SUKA KORI MA’AIKATAN SU DAGA AIKI

$
0
0

Dalilan Da Ya Sa Muka Kori Ma’aikatanmu Daga Aiki-MTN Da Airtel

           Dalilan Da Ya Sa Muka Kori Ma’aikatanmu Daga Aiki-MTN Da Airtel

Kamfanonin sadarwa na MTN da Airtel sun gurfana gaban kwamitin majalisar wakilan Nijeriya domin amsa korafin dalilian da ya sa suke sallamar ma’aikatansu babu gyaira babu dalili

 

Wajen mayar da martani ga wannan tuhumar da aka yi wa kamfanonin biyu, jami’i mai kula da harkokin ma’aikata na kamfanin MTN, Ajibola Opeoluwa-Calebs yashaidawa shugaban kwamitin harkokin sadarwa na majalisar wakilan Nijeriya, Honarabul Saheed Fijabi cewa a cikin mutane 368 da suka bar aiki a MTN a shekarar da ta gabata, ma’aikata 174 suka kora saboda sun gaza cika sharuddan kamfanin na tafiya da zamani a kimiyyar sadarwa.

 

Ya ce “Harkar sadarwa harka ce da ke samun ci gaba a kodayaushe a kimiyyance, amma wadancan ma’aikata da suka fuskanci kora ba su da kwarewar da za su iya aiki da sabon fasahar da aikin nasu ya zo da shi”

 

“Ragowar ma’aikata 194 kuwa su suka bar aiki akan ra’ayinsu”, in ji jami’in na MTN

 

“Har wa yau, MTN ta samar da guraben aiki wa mutane 150 don su maye guraben wadanda suka bar aiki ko aka kora saboda rashin kwarewa”

 

Mista Caleb ya bayyanawa ‘yan majalisar cewa MTN na nan na yin wani shirin na daukar mutane 240 nan ba da dadewa ba

 

Shi ma a nasa bayanin, jami’in harkokin ma’aikata na Airtel, Gbemiga Owolabi ya bayyana wa kwamitin majalisa cewa, a cikin shekara daya da ta wuce mutane 90 ne kawai suka bar aiki a Airtel. Cikin 90 din, 66 su suka rubuta takardar barin aiki bisa ra’ayinsu na kashin kansu, an kori 6 saboda samunsu da laifuka daban-daban sa’annan kuma an kori ma’aikata 14 sakamakon rashin kwarewa da gamsar da kamfani cewa za su iya aiwatar da aikin da aka daukesu su aiwatar

The post KARANJI KAJI: DALILAN DA YASA KAMFANIN MTN DA AIRTEL SUKA KORI MA’AIKATAN SU DAGA AIKI appeared first on MUJALLARMU.


KASAR MISRA TA HARAMTAWA IYAYE SANYWA ‘YA’YANSU SUNAYEN TURAWA

$
0
0

Kasar Misra Za Ta Haramtawa Iyaye Sanyawa ‘Ya’yansu Sunayen Turawa

Kasar Misra Za Ta Haramtawa Iyaye Sanyawa ‘Ya’yansu Sunayen Turawa

Majalisar dokokin kasar Misra ta na aiki akan wani kudirin doka da zai hukunta iyayen da ke sanyawa ‘yayansu sunan Turawa kamar su Mark, Lara, Sam da sauransu.

Dan majalisa Bedier Abdel Aziz wanda ya gabatar da kudirin ya bayyana cewa sanyawa ‘yaya sunayen turawa zai haifar da matsaloli ga al’ummar kasar da al’adunta.

Dayan dalilin da ya bayar shine, larabawa da yawa ba sa iya fadin sunayen turancin da kyau.

A karkashin kudirin, za a ci tarar iyayen da suka saba wannan doka dala 270 ko kuma a daure su na tsahon watanni 6.

Mutanen kasar da dama dai sun yi watsi da wannan kudiri, inda suke ganin shi a matsayin bata lokaci a wajen ‘yan majalisar.

Wasu kuwa haka suka ce sanyawa yara suna hakki ne na iyaye kuma za su iya yin yadda suka so.

Wannan dai ba shi ne karon farko da wata kasa ke haramta wasu sunaye ba. A 2014, kasar Saudiyya ta haramta sunaye 51 da suka hada Linda da Maya da wasu sunayen da ‘yayan sarauta kawai ake baiwa.

The post KASAR MISRA TA HARAMTAWA IYAYE SANYWA ‘YA’YANSU SUNAYEN TURAWA appeared first on MUJALLARMU.

A KARO NA BIYU HUKUMAR JAMB TA KASA TA SAKE BAIWA WASU DALIBAI DAMAR SAKE ZANA WATA JARABAWA

$
0
0

Hukumar JAMB zata sake gudanar da jarabawan ga wasu dalibai.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Akalla dalibai 62,140 ne zasu sake rubuta jarabawa shiga makarantun gaba da sakandare wato JAMB na bana,Shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede, yayi bayani a wata hira da manema labarai ranan Laraba cewa an shirya ranan 1 ga watan Yuli domin rubuta wani jarabawan.
    
Kana hukumar JAMB ta sallami wajajen rubuta jarabawa 24 bisa abubuwan da suka shafi kayan aiki. Sakamakon dalibai 62,140 da aka watsar ya kunshi 57,646 da ake zargi da satan amsa, 3,811 rashin rijista da wuri, da kuma 683 wadanda aka samu matsalan hoto.
Amma hukumar tayi watsi da sakamakon dalibai 2,052 da ake da yakinin sunyi satar amsa.
Yayi bayanin cewa daliban da ake baiwa daman sake rubuta an basu ne domin anyi satar amsa a wuraren da suka rubuta amma babu yakinin cewa kowannensu yayi satar.
JAMB ta jaddada cewa dalibai 1,722,236 ne sukayi rijisan jarabawan bana wanda shine adadin mafi yawa a tarihin jarabawar.

The post A KARO NA BIYU HUKUMAR JAMB TA KASA TA SAKE BAIWA WASU DALIBAI DAMAR SAKE ZANA WATA JARABAWA appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: SARKIN KANO SANUSI II YA BAYYANA ASALIN MATSALAR DATA DABAIBAYE NIJERIYA

$
0
0

Sarki Sanusi ya bayyana asalin matsalar dake damun Najeriya.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

A baya dai Sarki Sanusi ya yamutsa hazo kan batun siyasa da tattalin arziki Sarki Sanusi ya yi sabon tsokaci kan matsalar da Najeriya ke fuskanta Sarki Sanusi ya yi Allah-wadai da masu yada tsana a al’umma.
           
A tsokacin sa na baya-bayan nan, mai martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya ayyana matsalar kabilanci da bangaranci a matsayin babbar matsala daka iya hadiye kasar nan baki daya.
Sarkin ya yi tir da Alla-wadai da masu ingiza rikici da tsana ta kabilanci a tsakanin kabilun kasar nan.
“Dole mu bar bin abin da iyaye da kakanni suka fadi a zamanisu, na kin juna da kabilanci da bangaranci, idan a 1953 Sir Olaniwon yayi wata maganar kabilanci baro-baro, baya nufin muma na wannan lokaci sai munyi koyi da wannan”,
Sarkin ya wallafa a shafinsa na Instagram.Da alama dai Sarkin na bayani ne kan irin rarrabuwar kai da kabilanci hade da bangaranci da aka yi ta samu a lokutan mulkin mallaka da ma bayan samun ‘yancin kai, tsakanin manyar kasa, inda zaka ji mutum kamar Ahmadu Bello na fitar da kishinsa karara ga arewa, da nuna tsagwaron wariya ga wasu kabilun kasar nan.
Sarkin ya kara da cewa, ko kafin jihadin dan Fodio, kafin ma zuwan turawa, Hausawa na kashe kawunansu a cikin arewa, garuruwa irin su Zazzau, Kano da Hadejia na yakar junansu, zamani yayi da za’a dubi abin aga lokacin ya wuce, a rungumi juna a zauna tare a matsayin ‘yan Najeriya, a cewarsa.
Sarkin ya kara da cewa: “In ka duba zaka ga ana cewa Babagida ya lalata tattalin arzikin kasa, ba’a la’akari da su waye suke cikin gwamnatinsa a lokacin, sai kaji ana cewa wai anyi murdiya a zabe, amma ai ko Obasanjo da Maurice Iwu sunyi murdiya a 2007.”
Sarkin ya kuma yi tsokaci kan shugabanci, inda ya ce tun lokacin su Awolowo, ya zuwa yanzu, babu wani shugaba da ya kai irin kwazon iya mulkinsu, sai ma sata da wawaso tsakanin ‘yan siyasa.
Ya kara da cewa kuma satar batta da kabila, kowa ma yi yake.

The post KARANTA KAJI: SARKIN KANO SANUSI II YA BAYYANA ASALIN MATSALAR DATA DABAIBAYE NIJERIYA appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: ABINDA GWAMNAN KOGI YAHAYA BELLO YACE GAME DA DINO MELAYE

$
0
0

Sanata Dino bai samu tarbiyya na kwarai daga gida ba – Gwamna Yahaya Bello.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce rashin samun cikakken tarbiyya da ya dace ne ke sa sanata Dino Melaye yin abin da ya ga dama Wannan ya biyo bayan kira da Dino ya yi na kalubalantan gwamnan da ya fito ya bada bayanai akan yadda yake kashe kudaden jihar.
Haka zalika a ranar Laraba Dino ya yi ma gwamnan tatas a majalisa inda yace gwamnan bai san abinda ya keyi ba Wutar kiyayyan da ke tsakanin Sanata mai wakiltan Kogi ta Yamma Sanata Dino Melaye da Gwamnan jihar Yahaya Bello na ci gaba da ruruwa.
Bayan zargin gwamna Yahaya Bello da sanata Dino ya yi na cewa shine ya aika wasu bata gari domin su kashe shi a wani hari da aka kai masa lokacin da yake gudanar da wata zanga-zanga a jihar, ya kuma kalubalanci gwamnan da ya fito ya bada bayanai akan yadda yake kashe kudaden jihar.
Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, gwamnan Yahaya Bello ya ce rashin samun cikakken tarbiyya da ya dace ne ke sa sanatan yin abin da ya ga dama. “ Idan mutum bai sami tarbiyya na kwarai ba zaka ga ya zama fitina ga al’umma.
Idan kuma al’umma suka kasa canza shi sai kaga ya gagare su. Daga nan ne fa dole sai gwamnati ta sa hannu wajen seta shi.
” Ko da yake shima Sanata Dino ba kanwan lasa bane domin yayi wa Yayaha Bello tatas a majalisa ranar Laraba inda yace gwamnan bai san abinda ya keyi ba kuma ya roki majalisar da ta kafa dokar ta baci a jihar.

The post KARANTA KAJI: ABINDA GWAMNAN KOGI YAHAYA BELLO YACE GAME DA DINO MELAYE appeared first on MUJALLARMU.

ABIN TAKAICI: KASAR SAUDIYYA TA AIKOWA NIJERIYA DA DABINO AMMA AN SAIDA

$
0
0

Abin kunya: Saudi ta aikowa Najeriya dabino sadaka amma an saida .

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Kasar Saudi ta aikowa Najeriya sadakar dabino na azumi Sai ga shi yanzu ana saida wannan dabino a kasuwa Ministar kasar da tayi alkawarin za a rabawa ‘yan gudun hijira Wannan abin kunya sai ace da me yayi kama Najeriya dai ta kara buga abin kunya a idon Duniya.
              
An aikowa Najeriya sadaka amma an kai kasuwa domin a ci riba Saudi ta aikowa Najeriya ton 200 na dabino an saida Kwanakin baya kun ji cewa Ofishin Jakadancin Saudiya a Najeriya ya bayyana cewa kasar ta aikowa Najeriya tulin dabino domin buda baki.
            
Sai dai yanzu haka wannan dabino na yawo a kasuwa cikin Abuja ana saidawa,Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim Karamar Ministar harkokin kasar wajen Najeriya Ministar harkokin kasar waje Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim tayi alkawari da fari cewa za a raba kayan ne musamman ga ‘Yan gudun Hijira da ke Yankin Arewa maso gabas sai dai ba haka abin ya kasance ba.
Gwamnarin Tarayya ta bakin Ma’aikatar harkokin kasar wajen ta ba Kasar Saudiya hakuri inda tace wasu bata-gari ne su ka yi gaba da dabinon bayan an kai inda ya kamata a raba su domin su samu abin Duniya.

The post ABIN TAKAICI: KASAR SAUDIYYA TA AIKOWA NIJERIYA DA DABINO AMMA AN SAIDA appeared first on MUJALLARMU.

KAMFANIN MTN SUN KARA DANKON ZUMUNCI DA CUSTOMERS SUN SHIRYA MUSU GAGARUMIN BUDA BAKI A KANO

$
0
0

… sun hada buda baki domin customers a Kano

June 12, 2017 rana ce da Kamfani MTN suka ware domin kara dankon Zumunci tsakanin su da abokan cinikin su dake Kano, Muhammad Siddiqu wanda shine Chief Operation Officer ya jagoranci manya manya Shugabanin Kamfanin inda sukayi Buda baki tare da wasu abokan cinikayyar su a Kano.

Dan ganin cewa sun ci gaba da farantawa abokan cinikayyar su rai wajen hulda, Jami’an Kamfanin sun saurari wasu korafe korafe na wasu daga cikin musulman da suka halarci wannan buda bakin .

Zaman natsuwa cikin dakin taro na FABs Centre and Events wanda aka kawata shi da Kalar Kamfanin na MTN, Bakin sun samu ganawa da manya manya Shugabannin Kamfanin na MTN inda har suka musu tambayoyi sannan kuma suka bayyana ra’ayoyin su akan samfurorin kamfanin da kuma ayyuka a yayin da suke buda bakin.

A yayin da Shi COO, Muhammad Siddiqu yake jawabi ya bayyana cewa “a irin wannan mahimmin lokaci, Kamfanin MTN sunna sane akan cewa ya kamata suyi wa abokan cinikayyan su godiya sannan kuma su nuna musu irin soyayyar da suke musu. Munyi amfanin da damar wannan watan Ramadan mai albarka domin nuna wa Abokan cinikayyar mu musulmai.

Wannan buta bakin da muka shirya na daya daga cikin shirye shiryen mu na sauraren Abokan Cinikayyan mu da muka fara a shekarar da ta gabata, a dandalin daban daban cikin Garuruwan Lagos, Port Harcourt da Abuja. a kowa ne zama mukan tattauna mahimman Batutuwa misali Batutuwa akan Matakin da Kamfanin yake, jin Raayoyi akan Samfurori da kuma ayyuka. da kuma shawarwari akan yadda zamu bunkasa ayyukan da dai sauransu.

Kamar yadda Muhammad Siddiqu ya bayyana, “ wannan wani mataki ne da masu kamfanin suka dauka domin ganin sun kawo hanya ganawa da abokan cinikayyar su, dan jin yadda zamu iya bunkasa Samfurori da kuma ayyuka domin mu cika burin mu na kara dankon zumunci dan ganin mun inganta rayuwar su”.

Manya manya baki da dama sun halarci wannan gagarumin buda baki sannan kuma sun yabi kamfanin na MTN wajen kokarin inganta rayuwar mutanen Jahar.

 

The post KAMFANIN MTN SUN KARA DANKON ZUMUNCI DA CUSTOMERS SUN SHIRYA MUSU GAGARUMIN BUDA BAKI A KANO appeared first on MUJALLARMU.

‘YAN NIJERIYA KUNA SAKACI DA RASHIN LAFIYA SHUGABA BUHARI-INJI TSOHON MINISTAN INGILA

$
0
0

Tsohon dan majalisa a Ingila yace mutanen Najeriya suna sakaci da batun lafiyar Buhari.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Tsohon dan majalisar Ingila, yace saboda sakacin mutan Najeriya, shugaba Buhari na iya mutuwa amma a ninke su aki gaya musu yadda batun yake Ana dai jinyar Buhari a Ingila, amma ba wani wanda ya ga shugaban kasar har yanzu.

Babu ranar da aka saka cewa shugaba Buhari zai dawo Tsohon dan majalisar Ingila Eric Joyce, wanda yace hukumomin Najeriya sun rena talakawansu kan kin bayyana wa jama’a asalin bayani kan rashin lafiyar shugaba Buhari, ya ce cikin makonnin da aka shafe ba’a ga shugaba Buhari ba, tana iya yiwuwa ma ya mutu ne amma aka boye wa ‘yan Najeriya.

Eric Stuart Joyce ya ma ce shugaba Buhari ya mutu tun tuni, amma wai an ki a gaya wa mutanen Najeriya gaskiya ne, saboda raina talakawa da gwamnatin tayi.
A cewarsa, muddin ba’a fito an wa talakawa bayanin ko ina shugaban yake ba, talakawa ya kamata su yi bore su nemi jin bahasi. “Idan wannan shugaban ya mutu, ya zama mutum na uku daga arewa da ya mutu a kan karagar mulki, amma wani daga kudu ya gaje shi.” Ya kuma yaba da hazakar mukaddashin shugaba Osinbajo inda ya ce yana da zafin nama da iya aiki, wanda zai iya zama cikakken shugaba idan aka bashi cikakkiyar dama.
Eric Joyce dai ya zama bature daya tilo da ya sanya ido sosai kan yadda gwamnatin Najeriya ke tafiya.

The post ‘YAN NIJERIYA KUNA SAKACI DA RASHIN LAFIYA SHUGABA BUHARI-INJI TSOHON MINISTAN INGILA appeared first on MUJALLARMU.


WATA KUNGIYAR KWALLON KAFA A SPAIN TA KORI KOCIN TA BAYAN AN DOKE SU DA CI 25-0 A KARON FARKO

$
0
0

An sallami kocin wata kungiyar matasan kwallon kafa a Spaniya, bayan da aka doke su 25-0.

 

Kungiyar ta matasan Serrano ta raba gari da kocin inda ta ce kwallayen da aka zura musu a raga sun wuce tunani.

Rahotanni daga jaridun Spaniya sun ce Lauyan kocin ya ce ‘mai horarwar bai matsa wa matasan sai sun ci kwallo ba a karawar’.

‘Kocin ya umarci matasan su saka matsi zuwa tsakiyar filin wasa, inda suka dinga kai hari amma suka bar baya da baraka’ in ji Lauyan.

Karawar da suka yi ita ce ta karshe a kakar bana, inda suka kammala a mataki na karshe ba tare da maki ba, bayan da aka zura musu kwallo 247 a wasa 30 da suka yi.

The post WATA KUNGIYAR KWALLON KAFA A SPAIN TA KORI KOCIN TA BAYAN AN DOKE SU DA CI 25-0 A KARON FARKO appeared first on MUJALLARMU.

MUKADDASHIN SHUGABA KASA NA GANAWA TA MUSAMMAN DA SARKIN KANO SANUSI II A FADAR GWAMNATI

$
0
0

     Yemi Osinbajo na ganawa da Sarki Sanusi a Aso Rock.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Labarin da muke samu yanzu na nuna cewa Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo, na ganawa da mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Jaridar DailyTrust ta bada rahoton cewa an fara ganawar ne jim kasan bayan sarkin ya isa ofishin Osinbajo misalin karfe 2:40 na ranan.
Duk da cewa ba’a samu bayanan abubuwan da suke tattaunawa ba,Dandalin Mujallarmu.com ta samu labarin cewa yanada alaka da rikicin tsakanin matasan arewacin Najeriya da yan kabila Igbo na da tashe kwanan nan.

The post MUKADDASHIN SHUGABA KASA NA GANAWA TA MUSAMMAN DA SARKIN KANO SANUSI II A FADAR GWAMNATI appeared first on MUJALLARMU.

Ana Shirin Kammala Ciniki Tsakanin Manchester United Da Real Madrid

$
0
0

A cigaba da hada hadar saye da sayarwa da akeyi na ‘yan wasan kwallon kafa ta duniya, yanzu haka kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, ta kammala sayen dan wasan baya na Benfica, mai suna Victor Lindelof, a kan kudi fam miliyan 31.

A na shirin kammala ciniki tsakanin kungiyar Manchester United, da Real Madrid, kan sayen dan wasan Real, Alvaro Morata, a sati mai zuwa kan kudi fam miliyan 65.

Kungiyar Barcelona, ta sayi Marlon Santos, dan shekaru 21 daga Fluminense, na tsawon shekaru uku, Roma tace ya zamo dole Liverpool, ta biya fam miliyan 35.5 idan har tana son sayen dan wasanta Mohammed Salah.

Corentin Tolisso, ya Koma Bayern Munich, daga kungiyar Lyon, a kan kudi yuro miliyan 41.5. Westham tana zawarcin mai tsaron raga na kasar Ingila, maisuna Joe Hart a matsayin aro.

 

daga dandalinvoa.com

The post Ana Shirin Kammala Ciniki Tsakanin Manchester United Da Real Madrid appeared first on MUJALLARMU.

[KWALLON KAFA] Hada Hadar Zaratan ‘Yan Wasan Kwallon Kafa Na Duniya

$
0
0

A cigaba da hada hadar ‘yan wasan kwallon kafa da akeyi a yanzu haka dan wasan gaba na kasar Faransa mai taka leda a kungiyar Atletico Madrid Antoine Griezmann ya sake rattaba hannun a kungiyarsa ta Atletico har zuwa shekara 2022.

Zlatan Ibrahimovic mai shekaru 35 da haihuwa ya fara tattaunawa da kungiyar kwallon kafa ta LA Galaxy na kasar Amurka domin mai yuwar ya koma kungiyar da taka leda idan tattaunawar tayi kai.

Dan wasan gaba na kungiyar Liverpool Philippe Coutinho mai shekaru 25 da haihuwa yace akwai rikita rikita bisa harsashe da akeyi na komawarsa Kungiyar Barcelona.

Shi kuwa Alexis Sanchez na Arsenal ya nuna shakkunsa na komawarsa kungiyar Manchester City saboda wasu dalilai dan wasan yace yafi dacewa da ya Koma Bayern Munich.

Dan wasan gaba na Chelsea Diego Costa na shirye shiryen Komawa Kungiyar Atletico Madrid a matsayin aro zuwa tsakiyar kakar wasan badi domin ya dawo da martaban kulob din ganin halin da ta shiga na rashin sayen ‘yan wasa da aka hanata.

Kungiyar kwallon kafa ta PSG dake kasar Faransa ta shaida wa Barcelona da ta cire ranta wajan sayan Marco Verratti domin ba na sayarwa bane ko da nawa zata saya.

Barcelona dai ta saka yuro miliyan €100 don ganin ta sayo dan wasan.

 

daga dandalinvoa.com

The post [KWALLON KAFA] Hada Hadar Zaratan ‘Yan Wasan Kwallon Kafa Na Duniya appeared first on MUJALLARMU.

KARANTA KAJI: NASARAR BUKOLA SARAKI A KOTU TA KARYATA SHUGABA BUHARI-Inji Reno Omokri

$
0
0

‘Nasarar Bukola Saraki ta Karyata shugaba Buhari’ inji Reno Omokri.

Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Reno Omokri ya caccaki gwamnatin shugaba Buhari Ya zargi gwamnati da bangaranci da addinanci da kabilanci tsakanin yan Najeriya Reno Omokri, wanda tsohon hadimin tsohon shugaba Goodluck Jonathan, kan harkokin tashoshin sada zumunta na zamani, ya wallafa a shafinsa na facebook cewa lallai sharrin da shugaba Buhari ya kulla wa ‘yan adawa domin a ci zarafinsu.
    
A shafinsa na Facebook, Reno Omokri ya zargi shugaba Buhari da tsoma baki a harkokin ‘yan majalisu, inda ya ce ai ma yaki da cin hanci da ake cewa ana yi, duk bige ce.
A cewar sa: “Wai fadar gwamnati tace sallamar qarar da kotu tayi wa, wai a cewarsu, babban kuskure ne, ai kaji wannan kasan shirme ne.”
“Amma a lokacin da aka sallami wadanda suka kashe wata mata da aka ce tayi sabo a Kano bara, ai gwamnati bata kushe hukuncin ba,
” An dai dade ana jin duriyar Reno Omokri, wanda shi har yanzu bai shigo hannu ba domin yana zama ne a kasar Amurka.

The post KARANTA KAJI: NASARAR BUKOLA SARAKI A KOTU TA KARYATA SHUGABA BUHARI-Inji Reno Omokri appeared first on MUJALLARMU.

Viewing all 3050 articles
Browse latest View live


<script src="https://jsc.adskeeper.com/r/s/rssing.com.1596347.js" async> </script>