Dalilin Da Ya Sa Hukumar JAMB Ta Rike Sakamakon Jarrabawar Dalibai 76,925.
Marubuci:Haruna Sp Dansadau

Shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyade shi ya bayyana haka ga manema labarai a jiya Laraba a babban birnin tarayya Abuja.
Farfesan ya ce su na kan bincike akan lamarin, kuma da zaran sun kammala, za su fitar da sakamakon wadanda ke da gaskiya.
Ya kara da cewa, izuwa yanzu sun saki sakamakon mutane 1,606,901 a cikin 1,718,425 da suka zana jarrabawar.
“Sauran sakamako guda 80,889 kenan” inji farfesan “muna sane muka rike 76,925 saboda zargin magudi”
Ya ce sauran za su fito nan ba da dadewa ba
The post KARANTA KAJI: DALILIN DA YASA HUKUMAR JAMB TA KASA RIKE SAKAMAKON JARABAWAR DALIBAI 76,925 appeared first on MUJALLARMU.